Connect with us

News

Gwamnatin Tarayya Ta Gargadi Yan Kasuwa Kan Boye Kaya Da Kara Farashi A Lokacin Ramadan

Published

on

Akwai yiwuwar za’a fuskanci matsalar karancin abinci a Nijeriya

Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa NOA ta gargaɗi ƴan kasuwa da su guji ɓoye kayan abinci da kuma ƙara farashi ba bisa ƙa’ida ba a lokacin azumin Ramadan.

A cikin wata sanarwa da babban daraktan hukumar, Lanre Issa-Onilu, ya fitar a ranar Alhamis, ya bayyana cewa sun samu rahotanni kan yadda wasu yan kasuwa ke ɓoye muhimman kayan abinci da ake yawan amfani da su a lokacin azumi, domin su haifar da ƙarancin kaya a kasuwa da kuma ɗaga farashi.

Advertisement

Sabuwar Gobara Ta Tashi A Wata Kasuwa A Kano, Ta Ƙone Shaguna 50

Ya ce wannan dabi’a na kawo tangarda ga tattalin arziki, kuma ba ta da wata hujja, musamman a irin wannan lokaci da addinai ke jaddada tausayi, sadaukarwa da kuma sauke nauyin zamantakewa.

Advertisement

Shugaban NOA ya ƙara da cewa ɓoye kaya da gangan na kawo cikas ga ƙoƙarin da ake yi na daidaita tattalin arziki, haifar da tashin farashi tare da ƙara jefa iyalai cikin wahala a daidai lokacin da suke fuskantar ƙalubale.

Ya jaddada cewa yin kasuwanci cikin adalci da gaskiya wajibi ne, yana mai cewa daidaito da kuma rangwame a farashi sun yi daidai da ƙimar ƙasa da kuma koyarwar addinai.

Advertisement

 

Premier Radio

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending