News
Cutar Sanƙarau Ta Hallaka Yara 33 A Sakkwato
Gwamnatin Jihar Sakkwato ta tabbatar da mutuwar mutane 33 sakamakon ɓarkewar cutar sanƙarau a wasu sassan jihar, yayin da ake ci gaba da samun sabbin masu ɗauke da ita.
Kwamishinan Lafiya na jihar, Dakta Faruk Abubakar, ya ce an samu mutum 256 da ake zargin sun kamu da cutar a ƙananan hukumomi takwas cikin wata guda da cutar ta sake ɓulla.
Kano: ‘Yan Bindiga Sun Hallaka Mutum, Sun Yi Awon-Gaba Da Shanu Sama Da 400 A Gwarzo
A cewarsa, ƙaramar hukumar Sabon Birni ce ke kan gaba da mutum 63, sai Wamakko 60, sannan Shagari 51, Tambuwal kuma 33 da kuma Dange Shuni mai 26.
Ya bayyana cewa mafi yawan mace-macen sun faru ne a cikin al’umma kafin a fara kai marasa lafiya asibiti, sakamakon jinkirin neman magani da kuma ɗaukar cutar a matsayin ƙaramar matsala.
Domin dakile yaɗuwar cutar, gwamnati tare da haɗin gwiwar ƙungiyar kare lafiya ta Duniya Médecins Sans Frontières ta buɗe cibiyoyin killace masu cutar a Dogon Daji da Tambuwal.
Kana Jami’an lafiya sun ce ana ci gaba da karɓar sababbin marasa lafiya, duk da cewa waɗanda aka kai asibiti da wuri na samun sauƙi.
Masana lafiya sun danganta ɓarkewar cutar da cunkoso, zafi da kuma rashin zuwa asibiti da wuri, tare da buƙatar jama’a su rungumi allurar rigakafi da kuma tsaftace muhalli.
-
News3 days agoShekara Kwana: Shekaru 24 Kenan Da Hatsarin Jirgin Sama A Unguwar Gwammaja Dake Jihar Kano
-
News5 days agoKamfanonin Bada Bashi Ne Suka Cire N1.5bn Daga Albashin Ma’aikatan Kano — SSG
-
News4 days agoDr. Muhammed Musa Zango Ya Kaddamar Da Neman Takarar Sanatan Kano Ta Tsakiya A Jam’iyyar APC
