News
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Ƙarin Kuɗin Jarabawar WAEC Da NECO
Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta dakatar da shirin ƙara kuɗin rajistar jarabawar kammala sakandare ta WAEC da NECO da aka shirya fara aiwatarwa daga shekarar 2027, domin ba da damar ci gaba da tattaunawa da masu ruwa da tsaki a fannin ilimi.
A baya dai, Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya ta amince da ƙarin kuɗin rajistar jarabawar zuwa Naira 50,000 ga kowane ɗalibi, matakin da ya jawo ce-ce-ku-ce daga iyaye, malamai da sauran masu ruwa da tsaki. An bayyana cewa sabon tsarin zai maye gurbin tsoffin kuɗaɗen rajista na WAEC da NECO daga shekarar 2027.
Gwamnatin Legas Ta Kwace Baburan Okada Sama Da 300
Sai dai, bayan korafe-korafe da suka biyo baya daga ɓangarori daban-daban, gwamnatin ta sanar da dakatar da shirin domin gudanar da ƙarin tattaunawa kafin ɗaukar mataki na ƙarshe. Masana ilimi da dama sun nuna damuwa cewa karin kuɗin na iya hana ɗalibai masu ƙaramin ƙarfi damar ci gaba da karatu.
Tun da farko, ƙarin kuɗin jarabawar ya haddasa suka daga wasu manyan ‘yan siyasa da ƙungiyoyi, waɗanda suka bayyana cewa hakan zai ƙara yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a Najeriya.
-
News4 days ago
Pantami Da Yaransa Sun Fantama Min Ƙarya, Domin Babu Inda Na Ba Shi Haƙuri, Inji Hajiya Naja’atu Muhammad
-
News2 days ago
Jami’an NSCDC Sun Cafke Mutane Biyu Da Saniyar Da Ake Zargin Ta Sata Ce A Kano
-
News2 days ago
Gwamnatin Kano Ta Ayyana 1 Ga Satumba A Matsayin Ranar Hutun Bikin Takutaha
