News
NCDC na bincike kan baƙuwar cuta da ta ɓarke a Jihar Delta
Daga Yasir sani Abdullahi
Hukumar NCDC mai yaƙi da cutuka masu yaɗuwa a Najeriya ta ce ta ƙaddamar da bincike kan wata baƙuwar cuta da ta ɓulla a Jihar Delta da ke kudancin ƙasar.
Rahotanni na cewa a makon da ya gabata wani ɗalibi ya rasu tare da kwantar da wasu tara a asibiti sakamakon cutar a yankin Boji-Boji na Ƙaramar Hukumar Ika ta Arewa-maso-Gabas.
BBC ta rawaito cewa, cikin wani saƙo da ta wallafa a shafinta na Twitter, NCDC ta ce tana sane da wata cuta da aka ce ta ɓarke tsakanin ɗaliban sakandare.
NCDC ta ƙara da cewa tana haɗa hannu da Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya, da Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya, da kuma Ma’aikatar Lafiya ta Delta.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
