News
Mota Ta Kashe Sojoji 2 A Kaduna
DAGA KHADIJA ABDULLAHI MAHMUD
Sojoji biyu na Makarantar Horas da Dakarun Najeriya (NDA) sun rasa rayukansu bayan da wata motar kwashe shara ta murkushe su babur dinsu a Kaduna.
Lamarin, a cewar wani ganau, ya faru ne da sanyin safiyar ranar Talata a yankin Mando da ke Afaka a jihar.
KAROTA ta cafke wasu matasa da makamai da kayan-maye a kano
Ya ce, “Sojojin bayan faduwa a kan babur din ne suka fada wani rami a kan hanyar, sai motar da ke binsu a baya ta murkushe su.
“Lamarin gaba daya ya faru cikin kankanin lokaci wanda hakan ya sa aka yi rashin sa’a babu wanda ya iya ceto sojojin.”
An ce an garzaya da sojojin zuwa asibitin Dakarun Najeriya na 44 inda aka tabbatar da mutuwarsu.
Jami’in hulda da jama’a na NDA, Manjo Bashir Jajira, bai amsa kiran da wakilinmu ya yi masa ba a kokarin jin ta bakinsa.
DAILY TRUST
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
