Connect with us

News

Mota Ta Kashe Sojoji 2 A Kaduna

Published

on

 

DAGA KHADIJA ABDULLAHI MAHMUD 

 

 

 

 

Advertisement

Sojoji biyu na Makarantar Horas da Dakarun Najeriya (NDA) sun rasa rayukansu bayan da wata motar kwashe shara ta murkushe su babur dinsu a Kaduna.

 

Lamarin, a cewar wani ganau, ya faru ne da sanyin safiyar ranar Talata a yankin Mando da ke Afaka a jihar.

KAROTA ta cafke wasu matasa da makamai da kayan-maye a kano

 

Ya ce, “Sojojin bayan faduwa a kan babur din ne suka fada wani rami a kan hanyar, sai motar da ke binsu a baya ta murkushe su.

Advertisement

 

“Lamarin gaba daya ya faru cikin kankanin lokaci wanda hakan ya sa aka yi rashin sa’a babu wanda ya iya ceto sojojin.”

 

An ce an garzaya da sojojin zuwa asibitin Dakarun Najeriya na 44 inda aka tabbatar da mutuwarsu.

 

Jami’in hulda da jama’a na NDA, Manjo Bashir Jajira, bai amsa kiran da wakilinmu ya yi masa ba a kokarin jin ta bakinsa.

Advertisement

 

DAILY TRUST

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending