News
Har ila yau, EFCC ta sake bankado maboyar yan Yahoo, ta kama mutum 18 a Lokoja
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
A ci gaba da kokarin da hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC ke yi na dakile yawaitar zamba a yanar gizo wanda aka fi sani da ‘Yahoo-Yahoo’, rundunar shiyyar Ilorin na hukumar ta sake mika ragamar ta zuwa jihar Kogi inda aka kama wasu mutane 18 da ake zargin ‘Yahoo-Yahoo. Yahoo Boys a Lokoja, babban birnin jihar.
Wannan dai shi ne karo na biyu da ake gudanar da irin wannan aiki a jihar cikin watanni biyu da suka gabata. Jami’an hukumar EFCC shiyyar Ilorin sun kama wasu mutane 19 da ake zargi da damfara a cikin watan Yunin 2022 a wurare daban-daban a Lokoja.
Ya Guje Wa Matarsa Bayan Ta Haifi Tagwaye Sau 5 A Jere
Kamen na baya-bayan nan, wanda aka yi a ranar Laraba, 3 ga Agusta, 2022 ya biyo bayan bayanan sirri da Hukumar ta samu.
Daga cikin wadanda ake zargin akwai ‘yan uwa guda biyu – Bala Caleb Abdulkarim da Ayuba Bala. Sauran sun hada da Adebayo Olubunmi, Yusuf Salawu, Victor Yakubu, Victor Udeh, Abutu Francis, Moses Akeji, Aiyegbe ThankGod, Eniola Adeniji, Abraham Ayodele, Julius Omowale, Samuel Onojah, Saka Usman Ojo, Isaac Emmanuel, Yusuf Mohammed, Ibrahim Musa da Omaonu Ojochenemi Victor.
Binciken farko ya nuna cewa wadanda ake zargin suna aiki ne a matsayin kungiyar damfarar wadanda abin ya shafa.
Wadanda ake zargin ‘Yahoo-Yahoo Boys’, na da wasu abubuwa masu laifi a hannunsu da suka hada da manyan motoci guda biyar daban-daban, wayoyi da kwamfutoci.
EFCC
