News
Sha’aban Sharada ya fice daga APC, ya karbi tikitin takarar gwaman Kano a ADP
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Dan majalisar tarayya mai wakiltar karamar hukumar Birni daga jihar Kano, Sha’aban Ibrahim Sharada, ya fice daga jam’iyyar APC zuwa ta ADP, harma kuma ya samu tikitin takarar gwamnan Kano a zaɓen shekarar 2023 mai zuwa.
Daily Nigerian ta rawaito cewa, wata majiya ta tabbatar da cewa, hukumar zaɓe mai zaman kanta ta kasa INEC, ta tabbatar tsayawar Sha’aban takarar gwamnan Kano a jam’iyyar ADP, tare da wanda zai masa takarar mataimaki, Rabiu Bako.
Sha’aban dai yayi rashin nasara a hannun Nasiru Yusuf Gawuna a zaɓen fidda gwani na dan takarar gwamnan Kano na jam’iyyar APC, bayan zazzafan rikici da yayi da tsagin gwamna Ganduje karkashin shugabancin Abdullahi Abbas, har ya shiga tsagin G7 daga baya, kafin yanzu da ya fice daga jam’iyyar.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
