News
’Yan Daba Sun Kone Gidan ’Yan Shi’a A Kano
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Wasu bata-garin matass sun kone ofishin Kungiyar ’Yan Uwa Musulmi (IMN) ta mabiya Shi’a da ke unguwar Dorayi Babba a Karamar Hukumar Gwale a jihar Kano.
Lamarin ya faru ne sakamakon harin da suka kai wa gidan a kwanakin baya.
Yan Bindiga Sun Datse Hannu A Zamfara
A wata hira da shugaban ofishin kingiyar Dokta Suleiman Gambo, ya yi da ’yan jarida a Kano, ya ce wasu bata gari ne suka tsallaka katangar ofishin, suka kuma cinna wa ginin wuta.
Ya ce a sakamakon haka, an kone musu kayan da suka kai na mlilyan uku.
Shugaban ya ce sun kai karar faruwar lamarin ga baturen ’yan sanda na Dorayi Babba, a inda ya je da kansa shi da wasu manyan jami’ansa, suka kuma gane wa idonsu irin barnar da aka yi musu.
Ofishin kungiyar wata matattara ce ga ’yan kungiyar, inda suke gudanar da taruka, da karatuttukansu na addini da kasuwanci da kuma adana kayayyaki na bukatu a unguwar.
A cewar shugaban, kafin faruwar wannan lamari, an kai wa wasu daga cikin ’ya’yan kungiyar ta su hari a ranar biyu ga watan Agusta yayin da suke gabatar da wani taro, inda aka ji wa wasu mutane biyar ciwo tare da kona wata motarsu.
Wakilinmu ya tuntubi Kakakin Rundunar ’Yan Sanda ta Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, ya kuma ce bai samu rahoton afkuwar lamarin ba, amma zai bincika da kuma daukar matakin da ya dace.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
