Connect with us

News

Mun Baiwa Mutane 6,000 Tallafin Naira 20, 000 Kowannensu A Jihar Katsina -Sadiya Umar Farouq

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

 

 

 

 

Advertisement

 

 

Akalla mutane 6,000 ne suka karbi Naira 20,000 kowannensu a matsayin tallafin kudi a Katsina a wani bangare na kokarin gwamnatin tarayya na rage radadin talauci a tsakanin talakawa da marasa galihu a kasar nan. Kamar yadda Daily Trust ta ruwaito

 

Hakazalika, sama da iyalai 1,000 a jihar ne suka ci gajiyar abinci da kayan abinci a matsayin tallafin da gwamnatin tarayya ke yi ga wadanda ambaliyar ruwa ta shafa a jihar.

An kuma samun Bene Mai Hawa 7 Ya Danne Mutane a Nigeria

Advertisement

Ministar kula da jin kai da magance iftila’i da ci gaban jama’a Hajiya Sadiya Umar Farouq ce ta bayyana hakan a unguwar Mazoji da ke Daura, yayin da ta kaddamar da rabon kayayyakin tallafin.

 

Kana ta ce wasu mutane 500 sun ci gajiyar aikin jinya kyauta, inda aka yi masu maganin matsalolin ciwon ido daban-daban tare da baiwa marasa lafiya da suka amfana kyauta da magunguna da sauran kayayyaki masu mahimmanci kamar gilashin ido da ke taimakawa mutum wajen gani.

 

Ministan ya ce gwamnatin tarayya tare da hadin gwiwar gwamnatocin jihohi suna gudanar da tantance bukatu da suka shafi bala’in ambaliyar ruwa da ya rutsa da yawancin jihohin tarayyar kasar nan, da nufin tallafa wa wadanda abin ya shafa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending