Mahukunta a Pakistan sun ce babban tafkin nan da ke barazanar amabaliya ya fara ja da baya.
An yi wasu hanyoyin ruwa guda uku wadanda ko da ruwan ya yi ambaliya zai samu wurin wucewa.
DA ƊUMI-ƊUMI: An kama mai sansata wa tsakanin ƴan fashin daji da mutane, Tukur Mamu
Wani jami’i a yankin ya ce ana ci gaba da kwashe mutanen da ke kusa da tafki wadanda yawansu ya kai 125,000.
Pakistan na fuskantar ruwan sama kamar da bakin kwarya wanda ya haddasa ambaliyar ruwan da ba a taba ganin irinta ba a tarihin kasar.
A wata ziyara da ya kai yankin Sindh, firaiministan kasar Shehbaz Sharif, ya bayyana wajen a matsayin kogi, yana mai cewa irin asarar da aka yi a wajen abin ba dadi.
