Connect with us

News

DA ƊUMI-ƊUMI: Dalibai sun tare filin jirgin sama na Legas bisa zanga-zangar yajin aikin ASUU

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADEEN 

 

 

Advertisement

Ɗalibai, ƙarƙashin ƙungiyar dalibai ta kasa, NANS, ta rufe hanyoyin da ke zuwa filin jirgin sama na Murtala Muhammed da ke Ikeja a jihar Legas.

Ci gaban zanga-zangar wani mataki ne na nuna adawa da matakin yajin aiki da kungiyar malaman jami’o’i ke yi.

Advertisement

Duk da mamakon ruwan saman da a ke yi, ɗaliban sun jure sun fito, inda su ka haifar da cunkoson ababen-hawa a titin da ke kan hanyar zuwa filin jirgin, lamarin da ya sa matafiya da dama suka makale.

Gadar Mina-Bida Ta Karye Bayan Kwana 5 Da Gyara Ta

Advertisement

Jaridar The Nation ta lura da jami’an rundunar ƴan sandan jihar Legas, da jami’an RRS, da na ‘yan sandan filin jirgin saman Legas, da sauran jami’an tsaro suna nan a wajen.

Ɗaliban da suka gudanar da zanga-zangar na dauke da alluna da kwalaye, su na ta rera wakokin gwagwarmaya domin nuna rashin jin dadinsu kan matakin da gwamnatin tarayya ta dauka.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending