News
Ƙungiyar ASUU Ta Fara Haɗa Kan Mambobinta Domin Fara Yajin Aiki A Najeriya
Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU) ta fara hada kan mambobinta dake jami’o’in kasar nan domin fara yajin aikin kasa baki daya.
Kungiyar ta ce ta dauki wannan mataki ne bayan watsi da al’amuranta da gwamnatin tarayya ta yi duk da sanarwar da ta aika wa hukumomin da suka dace inda a ciki har da ministocin kwadago da ilimi.
Ƙungiyar SSANU Da NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Shugaban ASUU, Farfesa Chris Piwuna, a wata wasika da aka fitar ranar 5 ga Oktoba, 2025, ya bayyan cewa babu wani ci gaba da aka samu na gwamnati ta biya bukatunta duk da cewa sun dade suna janyo sabani tsakanin gwamnati da kungiyar.
Idan ba a manta ba a kwanakin da suka gabata ASUU ta bai wa gwamnati wa’adin kwanaki 14 don kammala yarjejeniyar da aka tsara tun watan Fabrairu, 2025 ko ta fara yajin aikin gargadi na makonni biyu idan ba a dauki mataki ba.
ASUU ta ce manufar yajin aikin ita ce tilasta gwamnati ta sanya hannu da aiwatar da sabuwar yarjejeniya, da kuma sake farfado da tsarin jami’o’in kasar domin gogayya da sauran kasashe.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
