News
Sarkin Lokoja ya rasu yana da shekara 80
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Daya daga cikin manyan sarakunan Najeriya, Maigari na Lokoja, Alhaji (Dr) Muhammad Kabir Maikarfi lll ya rasu.
Maigari, mai shekaru 80, ya rasu da yammacin jiya Laraba bayan ya yi fama da gajeruwar rashin lafiya a wani asibiti mai zaman kansa da ke Abuja.
Ya kasance ɗaya daga cikin sarakunan gargajiya mafi dad6ewa a jihar Kogi, inda ya hau karagar mulki a 1992.
Sakataren Majalisar Gargajiya na karamar hukumar Lokoja, Muhammed Nalado Usman ya tabbatar da rasuwar basaraken a wata sanarwa da ya fitar a daren jiya Laraba.
Sanarwar ta ce za a yi jana’izar marigayin a yau Alhamis a Lokoja da karfe 4 na yamma.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
