Connect with us

News

Shugabannin majalisa za su gana da Buhari kan yajin aikin ASUU

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

 

 

 

Shugabannin Majalisar Wakilan Najeriya za su gana da Shugaba Muhammadu Buhari game da batun yajin aikin malaman jami’a ƙarƙashin ƙungiyar ASUU, wanda suka shafe wata kusan bakwai suna yi.

Advertisement

 

Wata sanarwa ta ce Kakakin Majalisa Femi Gbajabeamila ya ce nan da ‘yan kwanaki za su fitar da rahoton tattaunawar da suka yi da shugabancin ASUU da zimmar bai wa Buhari “don ya samu wasu bayanai na daban” don ɗaukar matakin da ya dace.

Za Mu Sanya Wa Jam’iyyu Ido Kan Kudaden Yakin Neman Zabe — INEC

Lamarin na zuwa ne yayin da ofishin ministan shari’a ya ce zai duba ƙorafin ASUU kan batun tsarin biyan albashi na IPPIS da kuma UTAS, wanda shi ne babban batun da ya jawo yajin aikin.

 

A ranar Alhamis ne shugabannin majalisar suka gana da ASUU, inda ministan ƙwadago da shugabar ma’aikatan gwamnatin tarayya da sakataren gwamnati suka halarta da zimmar kawo ƙarshen yajin aikin.

Advertisement

 

“Za mu rubuta matsayarmu da shawarwarinmu mu kai wa shugaban ƙasa, abin da ya sa muka taru ke nan don neman mafita,” a cewar Mista Gbajabeamila.

 

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending