Connect with us

News

Wata Mata Ta Haifi ’Yan Biyar A Katsina

Published

on

Jarirai

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Wata mata ta haifi ’yan biyar a kauyen Doma da ke Karamar Hukumar Faskari ta Jihar Katsina.

Advertisement

 

Mai jegon, mai suna Hajara Shuaibu, ta haifi ’yan biyar din ne a ranar Larabar ko da ake daga bisani Allah Ya yi wa biyu daga cikinsu (mace da namiji) rasuwa, sauran ukun kuma na cikin koshin lafiya.

Advertisement

 

Kotun Daukaka Kara ta Najeriya ta umarci ASUU ta koma aiki ba bata lokaci

Advertisement

 

Binciken Aminiya ya gano a gida Hajara ta haifi wasu daga cikin yaran, kafin daga baya aka garzaya da ita Babbar Asibitin Funtuwa inda a nan ta haifi sauran ukun.

Advertisement

 

Mahaifin Hajara ya ce daga Asibitin Funtuwa sai aka tura su Asibitin Koyarwa na Tarayya da ke Katsina don ci gaba da samun kulawa.

Advertisement

 

Ya kara da cewa a baya, ’yarsa Hajara ta haifi tagwaye har sau biyu inda wannan karon kuma ta haifi ’yan biyar.

Advertisement

 

Ya ce wannan shi ne karon farko a tarihin kauyensu inda aka samu wata ta haifi ’yan biyar.

Advertisement

 

Shi kuwa mijin Hajara, Shuaibu Hussein, ya bayyana farin cikinsa da wannan baiwa da Allah Ya yi musu, amma ya nuna damuwa kan yadda za su yi fama da dawainiyar yaran kasancewarsu masu karamin karfi.

Advertisement

 

Don haka ya yi kira ga gwamnati da hukumomi masu zaman kansu da sauran masu hannu da shuni da su taimaka musu game da dawainiyar kula da yaran.

Advertisement

 

Ko a kwanan nan, an samu wata da ta haifi ’yan biyar kamar Hajara a Umuahia, babban birnin Jihar Abia, mai suna Oluomachi Lynda.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

DAILY TRUST

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending