News
Mutum uku sun mutu a fashewar bam kan gadar da ta haɗe Rasha da Crimea
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Wata fashewa mai girman gaske a kan gada mafi tsawo a Turai ta kashe mutum uku a yankin Crimea da Rasha ta ƙwace daga Ukraine a 2014.
A cewar masu bincike, mutanen na cikin wata mota ne da ke kusa a lokacin da wata a-kori-kura ta tarwatse a kan gadar, abin da ya rusa wani ɓangare na gadar da ke da titi da kuma layin dogo na jirgin ƙasa.
Farashin Abinci Ya Ragu A Duniya In Ji Majalisar Dinkin Duniya
Rasha ta ce za a sake buɗe sashen layin dogon – inda tankokin man fetur suka kama da wuta – a yammacin yau Asabar.
Gadar wadda ke haɗe Rasha da yankin na Crimea, an buɗe ta ne a 2018 kuma alama ce ta ƙwacen da Rasha ta yi ba bisa ƙa’ida ba.
“Duk wani abin da aka yi ba bisa ƙa’ida ba, ya kamata a rusa shi, duk abin da aka sace sai an dawo wa da Ukraine kayanta, duk inda Rasha ta mamaye sai an ƙwato shi,” a cewar Mykhailo Podolyak, wani mai ba wa shugaban Ukraine shawara.
Sai dai bai amsa ko Ukraine ɗin ce ta kai harin ba.
BBC
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
