
News
An yi bikin bude gida 804 da gwamnatin jihar Borno da hukumar UNDP suka gina
DAG MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Gwamantin jihar Borno tare da hadin gwiwar hukumar raya kasashe ta Majalisar Dinkin Duniya, sun kaddamar da bude gidaje 804 wadanda suka sake ginawa domin tsugunar da al’umomin Ngarannam a jihar.
Shugaban ma’aikatar fadar shugaban Najeriya Farfesa Ibrahim Gambari ne ya kaddamar da bude gine-ginen.
Jirgin yakin Rasha ya fado kan wani gida a birnin Irkutsk
Gwamna Zulum ya mika wa al’umomin gine-gine 360 da suka hadar da shaguna, da makarantu, da gidaje ga malaman makaranta, da jami’an tsaro tare da ginin ofishin ‘yan sanda daya.
Gwamnan jihar ya fada a cikin wata sanarwa cewa daga cikin gidajen 804, a yanzu an kammala 564.
Ya kara da cewa gwamnatin jihar za ta gina gida 304, a yayin da hukumar ta UNDP za ta gina gida 500.

A wata sanarwa da gwamnan ya fitar a shafinsa na Tuwita ya ce Farfesa Gambari ya bude gidaje 804 da hukumar UNDP da gwamnan jihar suka gina.
Haka kuma sanarwar ta ci gaba da cewa sun bayar da kyautar shanu 2,674, da tufafi da abinci da kyautar kudi naira 100,000 ga duk magidanci.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
