Connect with us

Entertainment

Kotu Ta Sa Ranar Yanke Hukunci Kan Karar Da Aka Shigar Da Hadiza Gabon

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Kotun Shari’ar Musulunci da ke zamanta a Magajin Gari, a Jihar Kaduna ta sa ranar 15 ga watan Nuwamban 2022 don zartar da hukunci a karar da aka shigar da fitacciyar jarumar Kannywood, Hadiza Aliyu Gabon.

 

Advertisement

Aminiya ta rawaito wani Bala Musa, ma’aikacin gwamnati ya kai karar jarumar bisa zargin kin aurensa bayan ya kashe mata kudin da suka kai har Naira dubu 396.

 

Advertisement

NDLEA ta kama mutum 130 kan miyagun kwayoyi a jihar Kaduna

Bala dai ya ce sun yi soyayya da jarumar kuma ta yi alkawarin aurensa.

Advertisement

 

Gabon dai ta musanta saninsa, inda ta ce ba ta taba haduwa da shi ba a rayuwarta.

Advertisement

 

A ranar Laraba ce Alkalin kotun, Mai Shari’a Malam Rilwanu Kyaudai, ya dage sauraren karar bayan wani babban lauya, Sulaiman Lere, ya roki kotu da ta ba shi dama ya tattauna da bangarorin biyu domin sasanta lamarin.

Advertisement

 

Lauyan wanda ya shigar da karar, Barista Nurudeen Murtala, ya goyi bayan shawarar sasantawa da Barista Lere ya yi, inda ya kara da cewa sulhu abu ne da Allah yake so, don haka ba za a yi adawa da shi ba.

Advertisement

 

A nasa bangaren, lauyan wanda ake tuhuma Barista Mubarak Sani, ya goyi bayan shawarar sasantawa amma ya roki kotun da ta saurari shaidun da ya gabatar kan wanda ya shigar da karar.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending