Connect with us

News

Mai ilimine Kadai zai,iya jogorancin karamar hukumar Dala…. bandirawo 

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Kwararre a fannin likitanci Kuma Dan kwakwarmaya a fannin ilimi Jigo a Jam’iyar Action Democratic Party ADP, dan takarar Majalisar jaha a Karamar Hukumar Dala Sagiru Usman Bandirawo yace Dala gidan ilmi ce, a don haka ne take bukatar mai ilmi inji dan kishin Dala

Advertisement

 

 

Advertisement

ya bayyana hakan ne yayin tattaunawa da jaridar Indaranka a jahar Kano

 

Advertisement

 

Kotu Ta Ci Maigadi Tarar N530,000 Kan Satar Na’urar Dumama Ruwa

 

Advertisement

Yana mai cewa kamar Hukumar Dala cibiya ce ta ilmi a jahar Kano.

 

Advertisement

 

Kuma yace karamar hukumar Dala tanada Al,umman da suke iyafin kowacce karamar hukuma yawa adan haka akeson a Sami mutum kwarare a fannoni daban daban

Advertisement

 

 

Advertisement

Ya ce jihar Kano na tunkaho da dan takarar Gwamnan jahar a jami’ar Action Democratic Party (ADP) Honorable Sha’aban Ibrahim Sharada OON

 

Advertisement

 

Bandirawo yace ilimi ne ya haifar da Honorable Sha’aban Ibrahim Sharada Don haka ne karamar hukumar dala ke bukatar Jagora mai ilmi. Ya cigaba da cewa yanzu gashi Allah ya ba dan takarar Gwamna wanda yake da mutukar kwaraiwa wajen ilimi, muna fatan Kanawa su yi karatun ta-nutsu su zaɓe shi domin tabbatar da ingancin rayuwarsu.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Bandirawo ya yi nuni ga jama’ar jahar kano akan fifikon da Allah (SWT) ya baiwa ilimi, inda yace, “Alqur’ani ya nunar da mu bisa ga fifiko da Allah (SWA) ya bawa ilimi. Shi ne ma ya sa Allah bai aiko Manzonni, tun daga Annabi Adamu har ya zuwa Annabi Muhammad har sai ya ilmantar da su gaba da kowa”.

Advertisement

 

Ya kara da cewa, “Allah Ya umurce mu, mu mika amanar mu ga wadanda za su iya rike mana ita. Zabe na shugabanni a dimokaradiyya Kuma mu baiw wanda aka zaba amana ne”. Saboda haka, tun da Allah da kansa ne yake bawa masu ilimi amanar bayin sa, ashe wajibi ne ga Jama’ar Jihar Kano su auna kafin su yi zabe”.

Advertisement

 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Ya yi kira ga matasa da mata da su guji siyar da Yancin,su akan kudi Kuma suyi karatun ta-nutsu wajen zaɓen wanda zai inganta rayuwarsu tare da kira ga matasa da su guji bangar siyasa da shaye-shaye domin kuwa kamar yadda ya ce bare-gurbin ‘yan siyasa ne ke ba matasa kwaya domin su cimma burinsu a siyasance.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending