Sports
DA ƊUMI-ƊUMI: Argentina ta lashe gasar cin Kofin Duniya
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
A gasar cin Kofin Duniya mafi armashi a tarihi, wacce a ka gudanar da ita a Qatar, Argentina ta samu nasara, bayan da ta doke France da bugun daga kai sai mai tsaron gida bayan an tashi 3-3.
Ka Kama Ƴan siyasar dake sayen Katin Zaɓe a hannun talakawa – SERAP
Lionel Messi da Angel Di Maria ne suka saka Albiceleste a gaba, kafin daga bisani kyaftin din nasu ya sake jefa kwallo a cikin karin lokaci, amma Kylian Mbappe ya ci wa Les Bleus kwallaye 3 rigis.
Emiliano Martinez ne ya sake zama gwarzon dan wasan Argentina a bugun daga kai sai mai tsaron gida, yayin da ya buge kwallaye biyu.
Argentina ta lashe gasar cin kofin duniya karon farko tun shekarar 1986, lokacin da Diego Maradona ya zira kwallaye a raga.
Wannan nasara ta Argentina ta zama cewa Messi ya lashe duk wata gada da ya taɓa buga wa a rayuwarsa ta kwallon kafa.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
