Connect with us

News

Damisa ta biyu ta tsere daga gidan kula da namun dawa

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Wata damisa ta tsere da safiyar Litinin daga wata gonar da ake ajiye da ita a Afrika ta Kudu, mako biyu bayan da wata damisar ta tsere.

Advertisement

 

Al’ummar Edenvale da ke lardin Gauteng sun ga wata damisa tana yawo a yankin, kamar yadda kafofin yada labarai na kasar suka ruwaito.

Advertisement

Daminar 2023: Ruwan Farko Ya Sauka A Kaduna

A farkon wannan watan wata damisa ta tsere daga wata gona a yankin Walkerville na lardin Gauteng inda ta kwashe kwanaki tana kai hare-hare har ta raunata wani mutum da wani kare da kuma wani alade kafin daga baya a harbe damisar.

 

Advertisement

 

Wata hukuma mai rajin kare dabbobi daga ketar da ake musu, NSPCA ta tabbatar da ganin damisar, ta kuma bukaci hukumomi su dauki matakan kama ta baya ga gargadin jama’a su killace dabbobinsu na gida.

Advertisement

 

Sai dai daga baya tashar yada labarai News24 ta sanar da an yi nasarar kama damisar, kuma an kai ta wani wurin da za a killace ta.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending