Connect with us

News

Gwamnatin jihar Kaduna za ta fara amfani da Whatsapp wajen tattara Kudin Shiga .

Published

on

DAGA MARYAM BASHIR MUSA 

 

Advertisement

 

Hukumar tattara kudin haraji ta Jihar Kaduna za ta fara amfani da shafin WhatsApp, da kuma tsarin biyan kudi na kananan wayoyin hannu wato USSD wajen karbar haraji.

Advertisement

 

Shugaban hukumar Dr Zaid Abubakar wanda ya bayyana hakan jiya Laraba a wani taron tattaunawa kan tara haraji, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito ya ce za su yi hakan ne domin saukaka hanyar biyan harajin.

Advertisement

Dubun Matar Da Ke Sayar Da Katin Zabe Ta Cika 

Dr Abubakar ya ce, amfani da kafar ta WhatsApp, wadda aka fi amfani da ita wajen sada zumunta da muhawara zai saukaka wa masu biyan haraji wahalar zuwa banki da sauran wuraren biyan haraji domin biya.

 

Advertisement

An shirya taron tattaunawar ne a tsakanin kungiyoyin kare fararen hula da wasu da suka jibanci haraji da mulki da hadin guiwar hukumar tattara haraji ta Jihar ta Kaduna da kuma kungiyar Christain Aid.

 

Advertisement

Ya bayyana cewa a tsarin za a bai wa duk wanda yake biyan haraji wata lamba ta musamman wadda zai rika amfani da ita wajen biyan ta wannan hanya.

 

Advertisement

Haka kuma ya ce za a yi amfani da tsarin aika kudi na USSD, wanda masu wayoyi kanana da ba a hada su da intanete suma za su iya biyan harajin cikin sauki da sauran abubuwa da suka danganci harajin.

 

Advertisement

Hukumar ta ce za ta bullo da wadannan tsare-tsare ne su fara aiki kafin karshen watan Maris da ke tafe.

 

Advertisement

 

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending