Connect with us

News

An yanke wa sojoji bakwai hukuncin kisa bayan tserewa daga fagen daga

Published

on

 

 

Advertisement

An yanke wa sojojin DR Kongo bakwai hukuncin kisa saboda ‘tsorata a gaban abokan gaba’ lamarin da ya sa suka gudu, a fagen daga da suke fafatawa da ‘yan tawayen M23.

 

Advertisement

Lamarin da kuma ya haifar tsoro da razani a zukatan al’ummar yankin.

An kashe mutum ɗaya a yayin faɗa ya ɓarke tsakanin ƴan APC da PDP a Jigawa

Advertisement

Ranar Alhamis ne sojojin suka wuce ta tsakiyar garin Sake, kilomita 25 yamma da garin Goma da ke gabashin ƙasar .

 

Advertisement

”Suna ta harbi a iska bayan da suka guje wa abokan gaba a fagen daga”, kamar yadda mai shigar da ƙara a kotun sojin ƙasar ya bayana wa kotu ranar Asabar.

 

Advertisement

Hukumomi a lardin Kivu sun ce sojojin masu muƙamin Kofur sun musanta zargin, kuma lauyansu ya ce za su ɗaukaka ƙara game da hukuncin.

 

Advertisement

Mai gabatar da ƙarar ya zarge su da janyo kisan kai, bayan da fararen hula biyu suka mutu wasu huɗu kuma suka samu munanan raunuka, saboda razanarwar da sojojin suka janyo wa mutane.

 

Advertisement

A baya-bayan nan dai dubban mutane ne suka tsere wa muhallansu a garuruwan Goma da Minova yayin da ‘yan tawayen M23 ke ci gaba kusantar garuruwan daga garin Masisi da ke yammaci.

 

Advertisement

A watan Nuwamban bara, kotun sojin ƙasar ta yanke wa wasu sojoji uku hukuncin kisa saboda ”guduwa a filin daga” a lokacin faɗa da ‘yan tawayen, lamarin da ya haifar da tsoro da razana da kuma tarwatsewar fararen hula.

 

Advertisement

A DR Kongo ana yanke hukuncin kisa, to sai dai rabon da a zartar da hukuncin tun shekarar 2003, a maimakon haka ana sassauta hukuncin zuwa hukuncin ɗaurin rai-da-rai.

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending