News
Tsohuwa Ta Kona Danta Da Iyalansa
Ana zargin wata tsohuwa mai shekaru 75 ta cinna wa danta, jikokinta biyu da kuma surukarta wuta a Jihar Ondo.
Ana zargin dattijuwar ta yi ajalin dan nata da iyalansa ne bayan ta watsa musu fetur sannan ta cinna musu wuta a cikin gidansu, lamarin da ya haddasa mummunar gobara.
Rahotanni na nuni da cewa abin ya faru ne a wani kauye da mai suna Aponmu da ke wajen garin Akure, babban birnin jihar.
Majiyarmu ta shaida mana a ranar Talata cewa an kai magidancin da iyalan nasa Cibiyar Lafiya ta Tarayya da ke Owo, inda likitoci suka tabbatar cewa shi da matarsa da daya daga cikin yaran sun rasu.
“Babban dan ne kadai ya rayu, shi ma din a yanzu haka yana cikin mawuyacin hali,” in ji shaidar.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
