Connect with us

News

Daliba Ta Rasu Ana Tsaka Da Daukar Lacca

Published

on

 

 

Advertisement

Dalibar mai suna Aminat Akanke Tajudeen ta rasu ne a ranar jajibirin bikin rantsar da su a matsayin sabbin daliban kwalejin.

 

Advertisement

 

Abokan karatun marigayiyar sun ce ranar Alhamis din da aka tsara bikin rantsar da su din ya zo daidai da zagayowar ranar haihuwar Aminat, amma ta rasu a ranar Laraba.

Advertisement

Sarƙaƙiya 12 da ke tattare da bashin da Najeriya ta ciwo, don raba wa talakawa tallafin tausar-ƙirjin fuskantar tsadar fetur daga watan Yuni.

Aminiya ta gano cewa Aminat ta riga karbo rigarta ta bikin rantsarwar, kafin mutuwarta bayan da ta yanke jiki ta fadi a aji.

 

Advertisement

 

Wani jami’in kwalejin ya ce an garzaya da Aminat zuwa asibitin kwalejin, amma ko kafin a isa rai ya riga ya yi halinsa.

Advertisement

 

Wata daliba mai koyon aikin jinya wadda kuma take cikin wadanda suka duba marigayiyar a asibitin, ta ce duk da cewa a mace aka kawo Aminat, sun tura su zuwa Babban Asibitin Ilorin don guje wa zanga-zangar dalibai.

Advertisement

 

Daga bisani dai an yi jana’iyar dalibar aka kuma binne ta bisa tsarin addinin Islama a makabartar Musulmi da ke Osere.

Advertisement

 

 

Advertisement

Mahaifin Aminat, Akanke ya shaida wa Aminiya cewa babu wata alamar matsala ko rashin lafiya a tare da mariygayiyar a lokacin da suka rabu.

Ya ce sai da suka yi doguwar hira da ita, sannan shi da kansa ya raka ta zuwa inda ta hau tasi ta tafi makaranta.

Advertisement

 

 

Advertisement

Jami’ar huld da jama’a ta kwalejin, Misis Abibat Zubair ta bayyana cewa an yi juyayin Aminat a taron rantsar da sabbin daliban kuma shugaban kwalejin da dalibai sun kai wa mahaifan Aminat ziyarar ta’aziyya.

 

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending