Connect with us

News

Mene ne bambancin yin Umrah cikin azumi da sauran lokuta

Published

on

 

 

Umrah kalma ce ta Larabci wadda ke nufin ziyara, kamar yadda Dakta Abubakar Sani Birnin Kudu, babban limamin Dutse da ke jihar Jigawa ya bayyana.

 

Malamin ya ce a shari’ance Umrah na nufin ziyarar ɗakin Allah (Ka’aba) da nufin yin ibada, wadda ta ƙunshi shiga halin Ihrami da Talbiya da Ɗawafi da Sa’ayi tsakanin Safa da Marwa da kuma aski.

An Kashe Mutum 6 A Zaben Ranar Asabar A Kano

Yin Umrah na ɗaya daga cikin ibadu mafiya tarin lada da al’ummar Musulmai ke yi domin samun gwaggwaɓan ladan da ke tattare da yinsa.

Advertisement

 

 

Matsayin Umara a addinin Musulunci

Dakta Abubakar Sani Birnin Kudu ya ce malaman duniya sun haɗu a kan ra’ayi ɗaya cewa umara abu da da aka shar’anta yinsa.

 

”Ma’ana abu ne da ya zo a shari’ance ana dalilin a ayi shi”

Advertisement

 

Sai dai malamin ya ce dangane da matsayinsa a shari’a an samu saɓanin malamai inda wasu ke ganin mustahabbi ne, kamar Imamu Malik da Abu Hanifa.

 

Sai kuma ra’ayin Imamu Ahmad bin Hambal da Imamu Shafi’i waɗanda suke ganin wajibi ne yin umara amma sau ɗaya a rayuwar mutum, ba kowacce shekara ba.

 

”Lallai Umrah tana cikin ibadu masu muhimmanci, don haka yana da kyau mutum ya samu ya yi a ko da sau ɗaya ne a rayuwarsa” in ji Malamin.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending