Connect with us

News

Dalibai mata da aka sace a Kaduna sun tsere daga hannun ‘yan bindiga

Published

on

 

 

Advertisement

 

Yan matan makarantar GSS Awon da ke karamar hukumar Kachia a jihar Kaduna na arewa maso yammacin Nijeriya sun tsere daga hannun masu garkuwa da mutane, in ji gwamnatin jihar.

Advertisement

 

Sanarwar da Kwamishinan Tsaron Cikin Gida na Jihar Kaduna Samuel Aruwan ya fitar ranar Talata, ta ce ‘yan matan, wadanda aka sace su ranar 4 ga watan Afrilu, sun tsere ne daga cikin dajin da ke tsakanin jihohin Kaduna da Neja.

Advertisement

Fintiri ya ci zaɓen gwamnan Adamawa

Sanarwar ta ce ‘yan matan sun yi tafiyar kwanaki kafin su samu mafaka a wani wuri da ba a ambata ba.

 

Advertisement

Bayan haka ne mutane suka ankarar da gwamnatin jihar wadda ta yi shirin kwashe yaran cikin gaggawa da hadin gwiwar sojoji.

 

Advertisement

“Masu garkuwa da mutanen sun yi ta neman ‘yan matan a cikin daji ba su same su ba don an riga an kwashe su,” a cewar sanarwar.

 

Advertisement

A halin yanzu suna wani wuri na soji inda ake ba su kulawar da ta dace, a cewar sanarwar.

 

Advertisement

Gwamnan jihar, Nasiru El-Rufai ya sharwaci ‘yan matan su kara dagewa kan neman ilimi don samun makoma mai kyau, bayan ya yaba da karfin halin da suka nuna wajen tserewa daga masu garkuwa da mutanen.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending