News
A akwai Fargabar Rasa Rayuka Yayin da Tankar Mai ta kama da wuta A Jos
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Wani kazamin hadarin motar daukar mai a birnin Jos da ke Jihar Filato ya yi sanadiyar rasa rayuka da kuma asarar dukiyoyi masu yawa.
RFI ya ruwaito cewa tankar mai ce ta kwace inda ta afkawa wasu ababen hawa kana ta kama da wuta, abin da ya yi sanadiyar samun gobarar.
Zakari ya ce motoci da dama sun kone, tare da rasa rayuka, yayin da aka fuskanci matsala wajen kashe gobarar saboda rashin isar motocin ’yan kwana-kwana da wuri.
Tinubu ya bar Najeriya zuwa Turai, kwana 19 Kafin a rantsar dashi
Bidiyon da shaidun gani da ido suka dauka sun nuna yadda wasu jama’a ke dibar ruwa da kuma kasa suna kokarin kashe wutar.
Wakilinnmu wanda ya tattauna da wata mata da ta bayyana masa bacewar yaranta biyu da kuma jami’in agaji na Red Cross da shaidun gani da ido, ya ce ya ga gawarwakin mutane 8 da gobarar ta ritsa da su.
An dai samu hadarin ne akan mararrabar hanyar da ta fito daga Jami’ar Jos inda ake da mahadar hanyoyin da suka tafi Bauchi da Zaria da kuma cikin garin Jos.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
