Connect with us

News

Gambari Ya Mika Wa Gbajabiamila A Matsayin Shugaban Ma’aikata

Published

on

DAGA  KAIRU BASIRU FULTAN

 

Shugaban ma’aikatan tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, Ibrahim Gambari, ya mikawa kakakin majalisar wakilai mai barin gado, Femi Gbajabiamila, ragamar mulki

Gambari ya rike mukamin daga 2020 zuwa 2023 bayan rasuwar magabacin sa Abba Kyari a watan Afrilun 2020.

Zaman wanda ya baje kolin takardar mika mulki ya gudana ne a ranar Litinin a fadar shugaban kasa da ke Abuja kuma shugaban kasa Bola Tinubu ya halarta.

Majalisar Dattawa ta amince da bukatar Tinubu ta nada mashawarta na musamman guda 20

A makon da ya gabata ne Tinubu ya bayyana nadin Gbajabiamila a matsayin shugaban ma’aikatan fadarsa, yayin da Sanata Ibrahim Hassan Hadejia, wanda tsohon mataimakin gwamnan jihar Jigawa ne aka nada a matsayin mataimakin shugaban ma’aikata.

Advertisement

Jim kadan bayan shugaban kasar ya nada Gbajabiamila a hukumance, dan shekaru 60 da haihuwa ya bayyana jin dadinsa a wata sanarwa da ya kawo karshen cece-kuce na makonni.

“Bayan shafe shekaru 20 da suka gabata a majalisar dokokin Najeriya, kuma bayan na lashe zabe karo na 6 a majalisar dokokin kasar, zan yi aiki tare da shugaban kasa wajen sauke babban aikin da ke gabansa domin zaman lafiya da ci gaban tarayyar Najeriya.

“Zan ba da mafi kyawuna lokacin da na hau ofis a ranar 14 ga Yuni 2023 kamar yadda aka nuna a cikin wasikar shugaban kasa,” in ji shi.

A matsayinsa na shugaban ma’aikata, Gbajabiamila ya fi mayar da hankali ne kan tafiyar da harkokin yada labarai da jama’a, yayin da yake ba shugaban kasa shawara kan batutuwa daban-daban.

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending