Connect with us

News

Majalisar Dinkin Duniya ta yi tir da kisan da aka yi wa wasu fararen hula Sudan

Published

on

DAGA KABIRU BASIRU FULATAN 

Majalisar Dinkin Duniya ta yi tir da kisan da aka yi wa wasu fararen hula da ke barin birnin El Geneina da ke yammacin Sudan

Advertisement

Ofishin kula da yancin ɗan adam na Majalisar ya zargi dakarun RSF da masu tayar da ƙayar baya na yankin da kisan fararen hular.

Hukumar shirya jarabawar shiga jami’o’i ta kasa (JAMB) ta sanya makin samun gurbin karatu a bana

Dakarun RSF sun shafe makonni masu yawa suna faɗa da sojojin ƙasar, lamarin da ya tilasta wa fiye da mutum 500,000 barin muhallansu.

Advertisement

Majalisar Dinkin Duniyar ta ambato wani shaida da ya samu tsallakawa zuwa ƙasar Chadi yana tabbatar mata da harin.

Ya ce da yawa daga cikinsu sun ga yadda aka kwantar da mutanen da ba Larabawa ba a ƙasa kafin daga baya a harbe su.

Advertisement

BBC Hausa ta rawaito cewa Sannan suka warwatsa gawarwakinsu a kan titi a kusa da kan iyakar ƙasar.

Kashe-kashen da ake yi yanzu a yankin Darfur, ƙari ne a kan rikicin da yankin ke ciki tun 2003.

Advertisement

Kawo yanzu akwai alamun da ke nuna cewa faɗan ƙabilanci na ƙaruwa a Sudan.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending