News
Gwamnatin tarayya za ta soma aiki da na’ura don karbar haraji daga ‘yan tireda
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Gwamnatin tarayya ta ce za ta soma aiki da kungiyar kananan ‘yan kasuwa domin karbar haraji daga miliyoyin ‘yan tireda a yunkurin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na kara fadada tattara haraji.
A wata sanarwa da Hukumar Tattara Haraji ta Nijeriya, FIRS, ta fitar a ranar Litinin ta ce tana kokarin hadin gwiwa da kungiyar kananan ‘yan kasuwa ta MATAN domin karbar haraji daga mambobinta.
Kwankwaso: Mutane Sun So Na Rushe Musu Gida Lokacin Ina Gwamna
Ta ce za ta mayar da hankali musamman wajen amfani da na’urori wurin karbar harajin.
Nijeriya na daga cikin kasashen da ake da karancin karbar haraji a duniya inda ake karbar kashi 10.8 cikin 100 kamar yadda FIRS ta bayyana.
Kashi 47 cikin 100 na kasafin kudin 2023 zai fito daga haraji da sauran bangarori na rance.
Kasar, wadda ta fi kowace karfin tattalin arziki a fadin Afirka, ta dauki gagaruman matakai wadanda suka hada da cire tallafin man fetur da cire takunkumi kan hada-hadar kudaden waje, a kokarin gwamnatin ta Tinubu na habaka tattalin arzikin kasar.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
