Connect with us

News

Gwamna Abba Na Jihar Kano Ya Dora Kwamishinoninsa A Matakin Gwaji Na Wata 6

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI 

 

Advertisement

Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano, ya sanya sabbin kwamishinonin da aka rantsar a matakin gwaji na tsawon watanni shida, daga nan kuma za a tantance gwazonsu bisa la’akari da yadda suke gudanar da ayyukansu.

Gwamnan ya ce idan aka tantance kwamishinonin da sukayi kwazo za a yaba musu sannan kuma za a sallami wadanda suka gaza.

Advertisement

Mai Juna Biyu Ta Gamu Da Ajalinta Saboda Yajin Aikin Likitoci A Jihar Nasarawa

Ya bayyana haka ne a yayin taron majalisar zartarwa ta jiha da ya jagoranta a gidan gwamnati.

A wata sanarwa da mai magana da yawunsa Hisham Habib ya fitar, an ruwaito gwamnan na cewa zai jagoranci tawagar sa ido da tantance ayyukan kwamishinonin da ma’aikatun su.

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending