News
Jami’an Tsaro Sun Hallaka ‘Yan Fashin Daji 60, Sun Ceto Mutum 29 A Bauchi
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi ya tabbatar da cewa jami’an tsaro sun kashe mutane 60 da ake zargin masu garkuwa da mutane ne tare da kubutar da mutane 29 a karamar hukumar Tafawa Balewa da ke jihar.
Mohammed ya bayyana haka ne a lokacin da ya kai ziyarar jajantawa al’ummar Lere da ‘yan bindiga suka kai musu hari cikin ‘yan kwanakin nan.
Ya ce an samu nasarar hakan ne ta hanyar hadin gwiwa tsakanin ‘yan sanda da ‘yan sa kai, da mafarauta.
Gwamnan ya ce rashin tsaro yana kara ta’azzara a jihar, kuma ya jaddada aniyar gwamnatinsa na kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Mohammed ya kuma bayar da gudummawar babura 30 da Naira miliyan 10 ga jami’an tsaro a yankin.
A wani labarin kuma Kotu ta soke cancantar shiga dan takarar jam’iyyar APC
Gwamnatin tarayya ta ce yanzu haka shirye-shirye sunyi nisa domin sauya akalar motoci har milyan 10 masu amfani da man fetir zuwa amfani da Gas nan da watanni 36 masu zuwa.
Karaminin ministan Mai, Ekperikpe Ekpo ne ya baiyana haka a yayin baje kolin mai da iskar gas na shekarar bana wanda ake gudanarwa a birnin Abu Dhabi na hadaddiyar daular larabawa.
A wata sanarwa da kakakinsa Louis Ibah ya fitar, ya baiyaan cewar a yanzu haka anyi kawance da kanfanoni masu zaman kansu domin kawo kayayyakin da za’a yi amfani dasu wajen sauya akalar motocin nan da watanni 9 masu zuwa.
Ya ce matakin wani yunkuri ne na inganta yin amfani da Gas a tsakanin motocin kasar a maimakon Man fetir da suka dogara dashi.
