Connect with us

News

Majalisar wakilai ta yi watsi da buƙatar Tinubu ta sayen jirgin ruwan shaƙatawa

Published

on

DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN

Majalisar wakilan Najeriya ta cire kuɗi naira biliyan biyar da aka ware a cikin ƙaramin kasafin kuɗin ƙasar domin sayen jirgin ruwan shaƙatawa na shugaban ƙasa.

Advertisement

An Dage Lokacin Ganawa Tsakanin Gwamnatin Tarayya Da Kungiyoyin Kwadago Na Kasa

Shugaban kwamitin majalisar kan kasafin kuɗ, Abubakar Bichi ne ya sanar da hakan yau Alhamis bayan sun amince da ƙaramin kasafin kuɗin na naira tiriliyan 2.17.

Advertisement

Bichi ya shaida wa manema labaru cewa kwamitin ya mayar da kuɗn zuwa ɓangaren bashin karatu na gwamnatin tarayya, inda a yanzu kuɗin da aka ware wa bashin ya kai naira biliyan 10.

Dama dai batun sayen jirgin ruwan shaƙatawan na shugaban ƙasa ya haifar da muhawara a tsakanin al’umma, inda mutane da dama suka soki lamarin.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending