News
Rundunar Yan Sandan Jihar Kano Sun Bukaci A Kauracewa Shiga Haramtaccen taro, Ko Zanga-Zanga
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta yi kira ga al’umma su kwantar da hankulansu, su kaucewa shiga duk wani nau’i na haramtaccen taro, ko zanga-zanga, ko tattaki da ka iya haifar da tarzoma.
Rundunar, a cikin wata sanarwa da kakakinta, Haruna Kaiyawa, ya fitar, ta ce sahihin bayanai da ke hannunta, sun ce wasu kungiyoyin magoya bayan wata jam’iyyar siyasa na amfani da kafafen yada sada zumunta, suna tara jama’a da shirin fitowa kan tituna domin nuna adawa da hukuncin da kotun daukaka kara ta yanke.
Ya ce kwamishinan ‘yan sandan, Mohammed Usaini Gumel, ya yi kira ga daukacin al’ummar da su kwantar da hankalinsu, su guji duk wani nau’i na taro, ko zanga-zanga, ko Tattaki.
Ya ce duk wanda ya yi yunkurin kawo cikas ga zaman lafiya a Jihar za a kama shi kuma zai fuskanci fushin doka.
A wani labarin kuma Mutum 547,774 Ne Suka Neman Aikin Dan Sanda A Nageriya
Tsohon Firaministan Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo, Augustin Matata Ponyo, ya janye daga zaben shugaban kasar da za a yi a watan gobe.
Ya ce yanzu zai marawa Moïse Katumbi, hamshakin attajiri kuma tsohon gwamnan yankin Katanga baya.
Wakilan manyan jam’iyyun adawa na Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo sun gudanar da tattaunawa a farkon makon nan kan yadda za a tabbatar da gudanar da zaɓe cikin adalci, da kuma gudanar da bincike kan yiwuwar ɗan takara na hadin gwiwa da zai kalubalanci shugaba Felix Tshisekedi.
Ponyo ya ce ya yi imanin sauran ‘yan takarar jam’iyyar adawa za su bi sahunsa na janyewa don goyon bayan Katumbi.
Dukansu sun yi aiki a zamanin tsohon shugaban kasa Joseph Kabila – Ponyo a matsayin firaminista sama da shekaru hudu da Katumbi a matsayin gwamnan lardin Katanga na tsawon shekaru tara.
Tshisekedi, wanda ke neman wa’adi na biyu, na cikin ‘yan takara da dama da suka ƙaddamar da yakin neman zabensu a hukumance ranar Lahadi, 20 ga watan Disamba.
-
News6 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News2 days ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News7 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
