News
Tinubu Da Shattima Zasu Kashe Sama Da Billiyan 15 Wajen Tafiye-Tafiye A Shekarar 2024
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Shugaban kasa, Bola Tinubu da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima da masu taimaka musu a fadar shugaban kasa, za su kashe kudi naira biliyan 15.961 wajen tafiye-tafiyen kasashen waje da na cikin gida a shekarar 2024.
Wannan adadi yana kunshe ne a cikin kudirin kasafin kudin shekarar 2024, wanda yanzu haka majalisar dokokin kasar ke nazari akai.
Budaddiyar Wasikar Majalisar matasan arewa zuwa ga Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu
Bayanin adadin ya nuna cewa shugaba Tinubu zai kashe zunzurutun kudi har Naira billiyan 7 da milliyan 630 na tafiye-tafiye, wanda ya kasance mafi yawan kudaden da za a kashe a tafiye-tafiyen kasashen waje.
Arewa Radio ta rawaito cewa Idan majalisar tarayya ta amince, zai kashe Naira biliyan 6.992 wajen tafiye-tafiye zuwa kasashen waje da kuma Naira miliyan 638.535 wajen tafiye-tafiye a cikin kasarnan.
Hakazalika, mataimakin shugaban kasa Shettima zai kashe jimillar Naira biliyan 1.847 a balaguron kasa da kasa.
A tsarin kasafin kudin, zai kashe Naira biliyan 1.229 wajen tafiye-tafiye zuwa kasashen waje da kuma Naira miliyan 618.399 a tafiye-tafiyen cikin gida.
A Wani labarin kuma Budaddiyar Wasikar Majalisar matasan arewa zuwa ga Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu
Wasu ‘yan Afirka ta Kudu 19 da suka makale a Gaza tun bayan barkewar yakin Hamas da Isra’ila a watan Oktoba sun koma gida lafiya.
Sun isa filin tashi da saukar jiragen sama na OR Tambo na birnin Johannesburg da yammacin ranar Talata, a cikin wani jirgin da ya taso daga birnin Alkahira na ƙasar Masar.
Da farko dai an kwashe su zuwa birnin Alkahira ta mashigar Rafah, bayan samun amincewar hukumomin Isra’ila.
Zane Dangor, babban darektan ma’aikatar harkokin wajen Afirka ta Kudu, ya ce hukumar za ta yi kokarin kwashe ‘yan kasar da har yanzu ke Gaza cikin koshin lafiya, amma bai bayyana adadin wadanda suka makale a can ba.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
