Connect with us

News

Rundunar Ƴan Sanda Ta Kama Waɗanda Ake Zargi Da Satar Shanu A Kaduna

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI

 

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta bayyana cewa jami’anta sun kama wasu mutane biyar da ake zargin barayin shanu ne tare da kwato shanu huɗu daga gurin wadanda ake zargin.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Mansir Hassan ne ya bayyana hakan a ranar  Litinin a Kaduna.

Cristiano Ronaldo ya kafa tarihin yawan kwallaye a 2023 a duniya

Ya ce an kama waɗanda ake zargin ne a garin Tafa da ke ƙaramar hukumar Kagarko a jihar.

Wikki Time ta ruwaito cewa “A ranar 30 ga Disamba, shekarar bara ne jami’an mu da hadin gwiwar jami’an Rundunar tsaro ta JTF su ka kama wani matashi ɗan kimanin shekaru 20 da ake zargi da aikata satar shanu”

Advertisement

Haka kuma ASP Mansir Hassan ya ce an samu wanda ake zargin da shanu guda hudu da ake zargin na sata ne.

Ya kara da cewa bayan ƴan sanda sun gudanar da bincike kan wanda ake zargin, ya amsa cewa manajan wata gona da ke garin Sabon Wuse ya ba shi amanar kiwon shanun.

“Babban wanda ake zargin ya ce sun hada baki ne da sauran mutane hudun da ake zargin sun sayar da shanun da suka sace,” inji shi.

Hassan ya ce wadanda ake zargin dukkansu suna hannun ‘yan sanda domin ci gaba da bincike kuma za a gurfanar da su a gaban kotu idan sun kammala bincike.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending