News
Gwamnatin Tarayya za ta fara bai wa ɗalibai lamuni – Ministan Ilmi
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa a cikin Janairu za ta fara sakin kuɗaɗen lamuni ga ɗalibai.
Ministan Ilmi Yusuf Sununu ne ya bayyana haka, tare da cewa har yanzu maganar fara biyan a cikin watan Janairu ma na nan.
Ma’aikatan Lafiya: Za Mu Hukunta Duk Wanda Aka Samu DaLaifi – Dr. Nagod
Sununu ya ce tuni ma an fitar da manhaja ta yanar gizo, inda dukkan ɗalibin da ke buƙatar lamunin zai shiga ya cika fam, matsawar ya cika sharuɗɗan da ake buƙata.
Ya ce shirin bayar da lamunin ya nan domin akwai shi a cikin kasafin 2024.
Sannan kuma ya ce Majalisar Zartaswa ta amince a kafa rassan makarantun wasu ƙasashen waje a nan Najeriya, domin a ƙara samun yawan ɗalibai masu shiga jami’o’i da yawa.
Ya ce hakan kuma zai zaburar da manyan makarantu da cibiyoyi wajen yawan yin bincike-binciken faɗaɗawa da zurfafa ilmi.
Wannan shiri dai an bijiro da shi ne domin rage wa ɗalibai raɗaɗin tsadar rayuwa, biyo bayan cire tallafin fetur, wanda haifar da tsadar abinci, kayan masarufi da tsadar zirga-zirgar sufuri baki ɗaya.
Yayin da gwamnatin tarayya ta yi wa ma’aikata ƙarin Naira 30,000 tsawon watanni huɗu zuwa shida, su kuma ɗaliban manyan makarantu za a ba su bashi domin rage barazanar matsalar rayuwa da kuma kuɗaɗen makaranta.
Sai dai kuma za a bada lamunin ne ga ɗaliban da suka fito daga gidajen masu iyaye masu ƙaramin ƙarfi.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
