Sports
Lauyoyin matar da ta shigar da Alves kara sun ce sun gamsu da hukuncin da kotun ta Barcelona ta yanke.
DAGA MUHAMMAD MUHAMMAD ZAHRADDIN
Lauyoyin dan wasan Brazil Dani Alves sun ce za su daukaka kara kan hukuncin da wata kotu ta yanke masa bayan da ta same shi da laifin aikata fyade.
Bayan dage takunkumin da ecowas tayi Jamhuriyar Congo na,son Karfafa Zumuntar Hadin Gwiwa da china
A ranar Alhamis kotun ta samu Alves da laifin yi wa wata mata fyade a wani gidan rawa a Barcelona, ta kuma yanke masa hukuncin daurin shekaru hudu da watanni shida a gidan yari.
Kotun Lardin Barcelona ta yanke wa tsohon dan wasan na Brazil da Barcelona dan shekaru 40 hukuncin ne bisa laifin yin fyade a ranar 31 ga Disamba, 2022.
Kotun ta yi la’akkari da cewa matar ba ta amincewa Alves ya sadu da ita ba, abin da ke nuni da cewa fyade ya yi mata.
Har ila yau, Kotun ta kuma umurci Alves da ya biya diyyar euro 150,000 ga matar, da kuma haramta masa zuwa gidan ta, ko kuma wurin aikin ta, ko kuma yin magana da ita ta kowace hanya har tsawon shekaru tara.
David Saenz wanda yana daya daga cikin lauyoyin da suka kare matar, ya ce, “sun gamsu da hukuncin.”
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
