News
Mazauna Chikun sun yi zanga-zanga kan harin ta’addanci a yankinsu
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Mazauna yankin Chikun cikin Ƙaramar Hukumar Goningora da ke Jihar Kaduna sun tare babbar hanyar Abuja zuwa Kaduna a yankinsu sakamakon zanga-zangar da suka gudanar a ranar Alhamis.
Jaridar Intelrigeon ta rawaito cewar, mazauna yankin sun shirya zanga-zangar ne domin nuna rashin jin daɗinsu da harin ta’addancin da ‘yan bindiga suka kai yankin.
Majalisar Dattawa ta sahale wa Shugaba Tinubu tsige wasu manyan jami’ansa
Zanga-zangar ta yi sanadiyar hana abubuwan hawa zirga-zirga a hanyar kamar yadda aka saba.
A cewar tashar Channels TV, mazauna yankin da dama ne aka yi awon gaba da su yayin da wasu sun jikkata sakamakon harin ‘yan bindiga a yankin a ranar Laraba.
Tashar ta ƙara da cewa, mutum biyu sun mutu sakamakon harin, lamarin da ya fusata jama’ar yankin wanda ya kai ga sun shirya zanga-zanga.
Harin na zuwa ne kimanin mako guda bayan da sojoji suka kashe gawurtaccen ɗan ta’adda, Boderi Isyaku da wasu mutanesa a yankin.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
