Connect with us

News

Lokaci yayi da Hukumar EFCC zata fara kame masu taimakawa ‘yan ta’adda da kudade-Rundunar sojin Najeriya

Published

on

DAGA YASIR SANI ABDULLAHI TUKUNTAWA 

Rundunar sojin Najeriya ta bukaci hukumar yaki da cin hanci da rashawa EFCC da ta bibiyi wadanda ke da hannu wajen daukar nauyin ta’addanci a kasar tare da chafke su.

Advertisement

Da yake jawabi hafsan tsaron kasar Janar Christopher Musa ya ce lokaci yayi da ya kamata hukumar EFCC ta fara amfani da karfin da doka ta bata wajen kama mutanen da ke da hannu a taimakawa masu ta’addanci da kudade.

Hukumar EFCC ta ɓallo wa Yahaya Bello ruwan zafi, ta saka sunan sa cikin harƙallar kuɗaɗen da aka gurfanar da ƙanin sa

Yayin da yake karbar bakuncin shugaban hukumar ta EFCC Musa, ya ce kamo wuyan masu taimakawa ta’addanci da kudade shine babban abinda zai kawo karshen hare-haren a Najeriya, kasancewar ayyukan laifin basa tafiya idan babu kudi.

Advertisement

Musa ya kuma jadadda cewa rundunar sojan Najeriya ba ta goyon bayan cin hanci da rashawa, kuma ba zata laumunci shigar sojoji cikin rashawa ba, don haka rundunar zata baiwa EFCC duk hadin kan da take bukata.

A nasa bangaren, Ola Olukoyede shugaban hukumar EFCC a Najeriya ya ce babu wata hukuma da bata da gudunmowar da zata baiwa Najeriya a fannin yaki da rashawa ba, don haka ya zama wajibi jami’an tsaro su san da wannan.

Advertisement

Ya kuma koka kan yadda ake samun cin hanci tsakanin jami’an tsaro, yana mai alakanta hakan da karuwar matsalolin tsaro a wasu lokutan.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending