Connect with us

News

Yadda Ɗan Shekara 12 Ya Bindige Ƙanin Sa Dan Shekara 6 Bisa Kuskure A Taraba – ‘Yan Sanda

Published

on

DAGA MARYAM BASHIR MUSA 

Rundunar ‘yan sandan jihar Taraba ta bayyana cewa wani yaro dan shekara 6, dan uwansa mai shekaru 12, ya harbe shi bisa kuskure a Jalingo babban birnin jihar Taraba. (PREMIUM TIMES ta boye sunayen yaran saboda kananan yara ne).

Lamarin ya faru ne da yammacin ranar Talata a garin Nukkai, a babban birnin jihar.

Al’ummar Allawa Da Ke Jihar Neja Na Tserewa Daga Gidajensu Bayan Janye Sojoji Daga Garin

Da yake jawabi ga manema labarai a ranar Alhamis a Jalingo, kwamishinan ‘yan sandan jihar, David Iloyanomon, ya ce an kama iyayen yaran tare da mika lamarin zuwa sashin binciken manyan laifuka (CID) na ‘yan sanda a jihar domin gudanar da bincike.

Ya ce akwai kuma irin wannan lamari na kisan kai da ya shafi yara kanana wanda kuma aka gayyaci iyaye da masu kula da su domin yi musu tambayoyi.

Ba za a iya tuhumar ƙananan yara kan laifin kisan kai ba. Shi ya sa aka tasa keyar iyaye da masu kula da yaran da suka bar bindigogin a inda yarannza su iya kaiwa ga su, an mika su zuwa CID na jihar domin gudanar da bincike mai zurfi.

Advertisement

Mazauna garin Nukkai sun ce lokacin da suka ji karar harbin, sun yi zaton masu garkuwa da mutane ne suka diran musu.

Wannan lamari dai ya faru ne makonni kadan bayan kashe yara uku a kauyen Didango Geit da ke karamar hukumar Karim-Lamido ta jihar sakamakon irin wannan ganganci da suka yi a tsakanin su a gidajen iyayen su.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending