News
Akalla Yara 19 Suka Rasu Sanadiyyar Kamuwa Da Cutar Kyanda A Adamawa
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
A kalla yara kanana 19 ne suka rasu sanadiyyar kamuwa da cutar Kyanda a karamar hukumar Mubi, dake Jihar Adamawa.
Kwamishinan lafiya na jihar Felix Tangwami ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN a Mubi ranar Asabar cewa sama da yara 200 ne suka kamu da cutar a karamar hukumar.
Yadda Ɗan Shekara 12 Ya Bindige Ƙanin Sa Dan Shekara 6 Bisa Kuskure A Taraba – ‘Yan Sanda
Ya ce an soma samun labarin barkewar cutar ce a garin Yola, inda cikin gaggawa aka tura jami’an lafiya da magunguna domin a taro cutar kada ta yi ɓarkewar da ba za a iya shawo kansa da wuri ba.
Ya kuma ba da tabbacin cewa za a mika yaran da suka kamu da cutar zuwa snyan asibitocin jihar domin a basu kula.
Premium Times ta ruwaito cewa Kwamishinan ya ce tawagar likitocin za su kuma nausa zuwa karamar hukumar Gombi inda aka sake samun bullar cutar.
A karshe Tangwami ya dora laifin kin kai yara asibiti a yi wa ‘ya’ya rigakafin citar tun farko ne yi sanadiyar samun ɓarkewar cutar a yankunan jihar.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
