News
Majalisar Dokokin Jihar Kano Ta Amince Da Dokar Gwajin Cutar Ƙanjamau Da Ta Sikila Kafin Aure
DAGAYASIRSANIABDULLAHI
Majalisar Dokokin jihar kano ta amince da dokar yin gwajin cutar kanjamau da ta Sikila da kuma sauran cututtuka kafin yin aure.
Da yake Jawabi akan kafa dokar, Shugaban Majalisar dokokin jahar kano Alhaji Jibril Isma’il Falgore, ya ce dokar za ta daƙile yaɗuwar cututtuka a tsakanin ma’aurata da yaɗa su ga iyali da ma al’umma baki ɗaya.
Emefiele Ya Kalubalancin Hurumin Kotun Jihar Legas Na Sauraron Shari’arsa
Har ila yau, dokar ta ba da damar yin gwajin cututtuka masu haɗari da wuyar magani kafin yin aure, tare da tanadin hukunci mai tsanani ga duk wanda yaƙi yin biyayya ga dokar.
Mataimakin Akawun Majalisar kuma babban Sakatare Alhaji Nasiru Magaji, ne ya gabatar da karatu na uku akan dokar kafin amincewa da ita a ranar Litinin.
