Connect with us

News

Kungiyoyin Fararen Hula 50 Sun Soki Janyewar Jami’an ‘Yan Sanda Daga Hukumar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa Ta Kano.

Published

on

DAGAV YASIR SANI ABDULLAHI 

Kungiyoyin farar hula sun nuna damuwarsu kan janyewar jami’an ‘yan sanda daga hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, inda suka soki lamarin

Hakan na zuwa ne yayi wani taron manema labarai da aka gudanar a Abuja yau.

Kungiyoyin sun ce janyewar jami’an ‘yan sanda kusan 40, masu kula da harkokin tsaro da bincike ba wai kawo cikas ga ayyukan hukumar ba ne, har ma da sanya ayar tambaya game da son kai da ‘yancin kai na hukumomin dake tabbatar da doka da oda.

Kotu ta baiwa EFCC izinin rufe asusun banki har guda 1,146

A cewarsu ana daukar matakin a matsayin wani yunkuri na dakile binciken cin hanci da rashawa da ake yi wa Abdullahi Umar Ganduje, shugaban jam’iyyar APC mai mulki na kasa kuma tsohon gwamnan jihar Kano.

Kungiyoyin farar hula sun kuma bayar da shawarwari don magance cin hanci da rashawa yadda ya kamata a Najeriya.

Advertisement

Sun kuma jaddada bukatar samun ‘yancin cin gashin kai da daidaito a bangaren shari’a, inda suka bukaci hukumar kula da harkokin shari’a ta kasa da ta sanya ido sosai kan mambobinta.

Sun kuma yi kira da a tabbatar da gaskiya da rikon amana a harkokin mulki, inda suka bukaci jam’iyyun siyasa da su yi tir da dakatar da mambobin da ke fuskantar zargin cin hanci da rashawa.

Bugu da ƙari Ƙungiyoyin sun yi kira ga shugabannin addini, shugabannin al’umma, da masu inganta ɗabi’a da kuma yaki da cin hanci da rashawa a cikin yankunansu.

An yi kira ga maido da ‘yan sandan da aka janye daga hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano da su saukaka ayyukan hukumar yadda ya kamata.

Kungiyoyin farar hula sun kuma jaddada aniyarsu na yaki da cin hanci da rashawa tare da yin kira da a dauki mataki na bai daya domin gina kasar da ba ta da cin hanci da rashawa.

A ranar 25 ga watan Afrilu ne babban sufeton ‘yan sandan kasar ya bada umarnin janye jami’an ‘yan sanda daga hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano. Matakin dai ya janyo suka da kuma kiraye-kirayen a bi diddigin ayyukan tabbatar da doka da oda da suka shafi yaki da cin hanci da rashawa.

Advertisement

 

Kungiyoyin sune kamar haka

 

 

1. Civil Society Legislative Advocacy Centre (CISLAC)

2. Human and Environmental Development Agenda (HEDA Resource Centre)

Advertisement

3. Resource Centre for Human Rights and Civic Education (CHRICED)

4. Centre for Information Technology and Development (CITAD)

5. African Centre for Media & Information Literacy (AFRICMIL)

6. Borno Coalition for Democracy and Progress (BOCODEP)

 

7. BudgIT Foundation

Advertisement

8. Corporate Accountability and Public Participation Africa (CAPPA)

9. State of the Union (SOTU)

10. Tax Justice and Governance Platform

11.Transition Monitoring Group (TMG)

12.Women in Media Communication Initiative (WIM)

13.Zero Corruption Coalition (ZCC)

Advertisement

14.Alliance for Credible Elections (ACE)

15.Centre Democracy and Development (CDD)

16. Accountability Lab, Nigeria

17. Centre for Journalism Innovation and Development (CJID}

18.Say NO Campaign – Nigeria

19.Femi Falana Chamber

Advertisement

20.Health of Mother Earth Foundation (HOMEF)

21.Socio-Economic Rights and Accountability Project (SERAP)

22. Good Governance Team

23.21st Century Community Empowerment for Youth Initiative

24. OCCEN-Kano

25. Mothers and Marginalised Advocacy Centre ( MAMA Centre)

Advertisement

26.Social Action

27.Centre for Transparency Watch

28.West Africa Civil Society Forum WASCSOF

29.Global Rights

30 African Centre for Leadership, Strategy & Development (Centre LSD)

31.Partners West Africa

Advertisement

32.Order Paper

33.Say No Campaign

34 Environmental Rights Action/Friends of the Earth, Nigeria. ERA

35.Center for Fiscal Transparency and Public Integrity

36.Amnesty International Nigeria

37. RULAAC – Rule of Law and Accountability Advocacy Centre

Advertisement

38. Connected Development (CODE)

39. Centre for Democratic Research and Training (CRDDERT)

40. Praxis

41.CLEEN Foundation

42.Spaces for Change

43.Abuja School of Social and Political Thought

Advertisement

44.Yiaga Africa

45.Policy Alert

46.Socio Economic Research and Development Centre

47.Procurement Observation and Advocacy Initiative

48.Media Rights Agenda

49.MEDIA INITIATIVE FOR TRANSPARENCY IN

Advertisement

EXTRACTIVE INDUSTRIES (MITEI)

50.Centre for Social Justice

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending