News
Kungiyoyin Fararen Hula 50 Sun Soki Janyewar Jami’an ‘Yan Sanda Daga Hukumar Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa Ta Kano.
DAGAV YASIR SANI ABDULLAHI
Kungiyoyin farar hula sun nuna damuwarsu kan janyewar jami’an ‘yan sanda daga hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, inda suka soki lamarin
Hakan na zuwa ne yayi wani taron manema labarai da aka gudanar a Abuja yau.
Kungiyoyin sun ce janyewar jami’an ‘yan sanda kusan 40, masu kula da harkokin tsaro da bincike ba wai kawo cikas ga ayyukan hukumar ba ne, har ma da sanya ayar tambaya game da son kai da ‘yancin kai na hukumomin dake tabbatar da doka da oda.
A cewarsu ana daukar matakin a matsayin wani yunkuri na dakile binciken cin hanci da rashawa da ake yi wa Abdullahi Umar Ganduje, shugaban jam’iyyar APC mai mulki na kasa kuma tsohon gwamnan jihar Kano.
Kungiyoyin farar hula sun kuma bayar da shawarwari don magance cin hanci da rashawa yadda ya kamata a Najeriya.
Sun kuma jaddada bukatar samun ‘yancin cin gashin kai da daidaito a bangaren shari’a, inda suka bukaci hukumar kula da harkokin shari’a ta kasa da ta sanya ido sosai kan mambobinta.
Sun kuma yi kira da a tabbatar da gaskiya da rikon amana a harkokin mulki, inda suka bukaci jam’iyyun siyasa da su yi tir da dakatar da mambobin da ke fuskantar zargin cin hanci da rashawa.
Bugu da ƙari Ƙungiyoyin sun yi kira ga shugabannin addini, shugabannin al’umma, da masu inganta ɗabi’a da kuma yaki da cin hanci da rashawa a cikin yankunansu.
An yi kira ga maido da ‘yan sandan da aka janye daga hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano da su saukaka ayyukan hukumar yadda ya kamata.
Kungiyoyin farar hula sun kuma jaddada aniyarsu na yaki da cin hanci da rashawa tare da yin kira da a dauki mataki na bai daya domin gina kasar da ba ta da cin hanci da rashawa.
A ranar 25 ga watan Afrilu ne babban sufeton ‘yan sandan kasar ya bada umarnin janye jami’an ‘yan sanda daga hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano. Matakin dai ya janyo suka da kuma kiraye-kirayen a bi diddigin ayyukan tabbatar da doka da oda da suka shafi yaki da cin hanci da rashawa.
Kungiyoyin sune kamar haka
1. Civil Society Legislative Advocacy Centre (CISLAC)
2. Human and Environmental Development Agenda (HEDA Resource Centre)
3. Resource Centre for Human Rights and Civic Education (CHRICED)
4. Centre for Information Technology and Development (CITAD)
5. African Centre for Media & Information Literacy (AFRICMIL)
6. Borno Coalition for Democracy and Progress (BOCODEP)
7. BudgIT Foundation
8. Corporate Accountability and Public Participation Africa (CAPPA)
9. State of the Union (SOTU)
10. Tax Justice and Governance Platform
11.Transition Monitoring Group (TMG)
12.Women in Media Communication Initiative (WIM)
13.Zero Corruption Coalition (ZCC)
14.Alliance for Credible Elections (ACE)
15.Centre Democracy and Development (CDD)
16. Accountability Lab, Nigeria
17. Centre for Journalism Innovation and Development (CJID}
18.Say NO Campaign – Nigeria
19.Femi Falana Chamber
20.Health of Mother Earth Foundation (HOMEF)
21.Socio-Economic Rights and Accountability Project (SERAP)
22. Good Governance Team
23.21st Century Community Empowerment for Youth Initiative
24. OCCEN-Kano
25. Mothers and Marginalised Advocacy Centre ( MAMA Centre)
26.Social Action
27.Centre for Transparency Watch
28.West Africa Civil Society Forum WASCSOF
29.Global Rights
30 African Centre for Leadership, Strategy & Development (Centre LSD)
31.Partners West Africa
32.Order Paper
33.Say No Campaign
34 Environmental Rights Action/Friends of the Earth, Nigeria. ERA
35.Center for Fiscal Transparency and Public Integrity
36.Amnesty International Nigeria
37. RULAAC – Rule of Law and Accountability Advocacy Centre
38. Connected Development (CODE)
39. Centre for Democratic Research and Training (CRDDERT)
40. Praxis
41.CLEEN Foundation
42.Spaces for Change
43.Abuja School of Social and Political Thought
44.Yiaga Africa
45.Policy Alert
46.Socio Economic Research and Development Centre
47.Procurement Observation and Advocacy Initiative
48.Media Rights Agenda
49.MEDIA INITIATIVE FOR TRANSPARENCY IN
EXTRACTIVE INDUSTRIES (MITEI)
50.Centre for Social Justice
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
