News
Bayan Yi Wa Dokar Masarautar Kano Gyaran Fuska, An Jibge Jami’an DSS A Fadar Sarkin Kano.
DAGA MUHAMMAD BASHIR MUSA
Rahotanni na nuni da cewa an jibge jami’an Hukumar DSS a fadar Mai Martaba Sarkin Kano Alhaji Aminu Bayaro.
Bayan yi wa dokar da ta samar da sabbin masarautu a jihar tare da rushe masarautun da tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje ya kirkiro.
Ƙungiyar Ƙwadago Ta NLC Ta Sake Fatali Da Tayin N57,000 A Matsayin Mafi Ƙarancin Albashi
Wannan na zuwa ne bayan zama da majalisar ta yi a yau Alhamis tare da yin duba a kan dokar da ta kirkiro sabbin masarautun.
Tun da farko tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Umar Ganduje ne, ya yi amfani da dokar wajen tsige Sarkin Kano Muhammadu Sanusi II, Sarkin Kano na 14 a 2020.
Shugaban masu rinjaye kuma wakilin mazabar Dala, Hussien Dala ne, ya gabatar da kudirin gyara dokar a yayin zaman majalisar na ranar Talata.
Sai dai an wayi gari babu sarki mai ci a Jihar Kano bayan majalisar dokoki ta tsige sarakunan Kano, Bauchi, Gaya, Karaye da kuma Rano
