News
Yajin Aiki: Gwamnatin Nijeriya za ta gana da ASUU a yau Talata
Daga kabiru basiru fulatan
Da alama dai yajin aikin gargaɗi da Ƙungiyar Malaman Jami’a ta Ƙasa, ASUU ta fara ba zai kai wata ɗaya kamar yadda ta ɗauki aniya ba, bayan da Gwamnatin Nijeriya ta yi wuf ta fara yunƙurin daƙile wannan mataki na ƙungiyar.
Tuni ma dai gwamnatin, ta bakin Charles Akpan, Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a da Labarai na Ma’aikatar Ƙwadago da Ɗaukar Aiki, ya baiyana a yau Litinin a wata sanarwa.
Ya ce Ministan Ƙwadago da Ɗaukar Aiki, Chris Ngige ne zai gana da shugabannin ASUU ɗin da wasu masu ruwa da tsaki a ma’aikatun gwamnati.
Ya ce za a yi ganawar ne a yau Talata da ƙarfe 1 na rana a ofishin Ministan.
-
Uncategorized6 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News5 days ago
Aƙalla Mutane 40 Sun Mutu Bayan Kifewar kwale-kwale A Sokoto
-
News23 hours ago
Pantami Da Yaransa Sun Fantama Min Ƙarya, Domin Babu Inda Na Ba Shi Haƙuri, Inji Hajiya Naja’atu Muhammad
