Connect with us

News

APC ta sanya sabuwar ranar da za ta yi babban taro

Published

on

FB IMG 1645507075630
Spread the love

Daga yasir sani abdullahi

 

 

Advertisement

Kwamitin Riƙo na Jam’iya mai mulki ta APC ya sanya 26 ga watan Maris a matsayin ranar babban taro na jam’iyar.

John Akpankudohede, Sakataren jam’iyar na ƙasa, shi ne ya baiyana hakan ga manema labarai jin kaɗan bayan wata ganawar sirri a Abuja a jiya Litinin.

Akpankudohede ya ce bayan da a ka tattauna, Kwamitin Riƙo na jam’iyar ya sahale cewa tun ranar 24 ga watan Febrairu za a fara shirye-shiryen taron inda zai ƙare a ranar 26 ga watan Maris a filin Eagles Square.

Advertisement

Ya kuma ƙara da cewa kafin babban taron, jam’iyar ta amince da yin taruka na shiyya-shiyya.

Ya kuma ce za a bi tsare-tsare da jadawalin lokaci da jam’iyar ta tsara wajen aiwatar da taron.

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *