News
Atiku Ya Jajantawa Shugaba Tinubu Bayan Da Yayi Kudungula A Cikin Motar Da Yake Kokarin Hawa
DAGA YASIR SANI ABDULLAHI
Dan takarar da shugaba Tinubu ya kayar a zaɓen 2023, Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP, ya ce yana jajantawa Bola Tinubu dangane da zamewar da ya yi, a ranar Laraba.
“Ina matukar jajantawa shugaba Bola Tinubu dangane da ɗan hatsarin da ya samu a lokacin da yake ƙoƙarin zagaya masu fareti na bikin ranar dimokuraɗiyya.
“Ina fatan dai lafiya lau” in ji Atiku.
A baya-bayan nan dai an ga yadda tsohon mataimakin shugaban ƙasar, Atiku Abubakar ke ƙara ƙaimi wajen yin hamayya ta fuskar sukan abubuwan da yake ganin gwamnatin shugaba Tinubu ba ta yi daidai ba, kamar yadda jaridar BBC Hausa ta bayyana.
-
News2 days ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News2 days ago
Zaben 2027: INEC Ta Amince Da Atiku Abubakar, ‘Yan Takarar ADC 470
