News
Gwamnatin Kano Ta Ba Da Umarnin Fitar Da Sarki Aminu Daga Fadar Nassarawa
DAGA KABIRU BASIRU FULATAN
Gwamnatin Kano ta bayar da umarnin fitar da Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero daga karamar fada ta Nassarawa da yake zaune a cikinta.
Gwamnatin ta bai wa kwamishinan ’yan sandan jihar wannan umarni tana mai cewa akwai kwaskwarima da za ta soma yi wa ginin fadar nan ba da jimawa ba.
Babbar Magana: An Sace Wata Mata Mai Juna Biyu A Hanyar Zuwa Asibiti
Kwamishinan Shari’a kuma Lauyan Ƙoli na Jihar Kano, Barista Haruna Isa Dederi ne ya bayar da wannan sanarwar yayin wani taron manema labarai da ya gudana a yau Alhamis a Fadar Gwamnatin Kano.
Wannan dai na zuwa ne bayan hukuncin da wata Babbar Kotun Tarayya da ke jihar ta yanke a yau dangane da taƙaddamar Masarautar Kano.
Details soon
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
